DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ku karbo Nijeriya daga hannun dattijan da ke shugabancin kasar – Femi Falana ya shawarci matasa

-

Fitaccen lauya mai rajin kare hakkin dan’adam, Femi Falana, SAN, ya shawarci matasan Nijeriya da su karbo kasar daga hannun dattijai ta dawo hannunsu.
Dan gwagwarmaya Falana ya bayar da wannan shawara ne a birnin Legas, yayin taron shekara-shekara karo na shida na jagorancin matasa, wanda aka lakaba wa suna ‘Resilience, Innovation, Social Responsibility and Entrepreneurship (RISE 2025).
Falana ya ce abubuwa ba su kasance kamar yadda suke a da ba, saboda haka ya zama wajibi matasa su kwato kasarsu kuma su sake fasalta ta yadda ya kamata.
Ya kara da cewa matasa suna shan wahala sakamakon halin da kasar ta shiga, saboda haka akwai bukatar matasa su tashi tsaye don zage damtse su yi abin da ya kamata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon kwamishinan Ganduje ya soki gwamnatin Abba bisa zargin sayar da filin makarantar

Tsohon kwamishinan ilimi na a zamanin Ganduje, Muhammad Sanusi Sa'id Kiru, ya soki matakin gwamnatin Abba Kabir Yusuf na mayar da Makarantar Sakandare ta ‘Yan...

Hukumar zabe za ta hada kai da majalisar wakilan Nijeriya domin gudanar da sahihin zabe

Shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, Farfesa Joash Ojo Amupitan, ya bayyana aniyarsa ta yin aiki tare da Majalisar Dokoki domin tabbatar da gudanar da sahihin...

Mafi Shahara