Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiZaman lafiya ya dawo a kananan hukumomi 13 na jihar Katsina -...

Zaman lafiya ya dawo a kananan hukumomi 13 na jihar Katsina – Gwamnati

Dikko Umar Raɗɗa 

Mataimakin Gwamnan jihar Katsina Alhaji Faruq Lawan Jobe, ya ce gwamnatin jiha ta yi kokari ta maido da zaman lafiya a kananan hukumomi 13 cikin 22 da ke fama da matsalar tsaro a jihar.

Jaridar This day ta rawaito cewa Faruq Jobe na magana ne a gaban ‘yan jarida, inda ya ce an samu wannan nasarar ne ta dalilin ayyukan jami’an sa kai na ‘Community Watch Corp’ da gwamnatin ta kirkiro, hadin guiwa da sauran jami’an tsaro a jihar.

Daga cikin kananan hukumomin da tsaron ya fara inganta, a ta bakin mataimakin Gwamnan jihar, akwai Batagarawa, Dutsinma, Bindawa, Kusada, Funtua, Danja, Bakori, Malumfashi, Kafur, Musawa, Ingawa, Charanci da Matazu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata