Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiINEC ta shirya gudanar da zabukan cike gurbi a Kano

INEC ta shirya gudanar da zabukan cike gurbi a Kano

Hakan ya fito daga bakin kwamishinan Zabe na Jihar Malam Abdu Zango, yace an shirya yin zaben ne ranar 3 ga watan Fabrairu.

A cewarsa wuraren da za a gudanar da zabukan sune Kunchi da Tsanyawa, Kura da Garun Malam sai Rimin Gado da Tofa.

Kwamishinan ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi da masu ruwa da tsaki a hedikwatarta da ke jihar a yau Talata.

Ya kara da cewa za a yi amfani da tsarin tantance masu kada kuri’a na Bimodal BIVAS a yayin sake gudanar da zabukan da nufin tabbatar da sahihin zabe.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata