DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima zai wakilci shugaba Tinubu a kasar Senegal wajen bikin cika shekara 65 da samun ‘yancin kan kasar

-

Kashim Shettima

 Mataimakin shugaban kasar Shettima ya bar Abuja ne zuwa Dakar domin ya wakilci shugaba Tinubu a wajen bikin cikar Senegal shekaru 65 da samun ‘yancin kai.

Kasar Senegal na bikin ranar samun ‘yancin kai a ranar 4 ga watan Afrilun kowace shekara, inda ake bikin ‘yancin kai daga turawan mulkin mallaka na Faransa a shekara ta 1960.

Google search engine

Ranar dai ta kasance cikin alfahari da al’ummar kasar, tare da shagulgula, da yin fareti da wasanni na al’adun kasar.

Halartar mataimakin shugaban kasa a taron na shekara-shekara, don girmama goron gayyatar da shugaban kasar Senegal, Bassirou Diomaye Faye ya yi wa shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya biyo bayan kyakkyawar alakar da ke tsakanin Nijeriya da Senegal.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi ganawar sirri da sabbin hafsoshin tsaro a Abuja

Taron, wanda ya gudana kwanaki uku bayan sanar da sabbin nade-naden, shi ne karo na farko da shugaban kasa ya gana da manyan hafsoshin rundunonin...

Paul Biya ya yi wa masu zanga-zangar sakamakon zabe shagube a Kamaru

Shugaban ƙasar Kamaru, Paul Biya, ya yi shagube ga rikicin siyasar da ke faruwa bayan ayyana shi a matsayin wanda ya lashe sakamakon zaɓen shugaban...

Mafi Shahara