Sunday, April 5, 2026
HomeKetareSojoji sun yi ikirarin yin sabon juyin mulki a Gabon

Sojoji sun yi ikirarin yin sabon juyin mulki a Gabon

https://drive.google.com/uc?export=view&id=1g3szG8W_wref_Zv6KR5OQS-4reXtKAj4
Wani gungun manyan jami’an sojin kasar Gaban ya bayyana a kafar yada labaran kasar ta Gabon24, inda ya sanar da karfe iko da hannun gwamnatin Ali Bango.
Kafar yada labaran Aljazeera ta ce sojojin da suka ce sun kifar da gwamnatin ta dimukuradiyya a safiyar Larabar nan sun ce matakin nasu ya biyo bayan mummunan magudin zaben da aka tabka a zaben shugaban kasa na makon da ya gabata da ya bai wa Shugaba Bango karin wa’adin mulki bayan kwashe shekaru 14 a kan karagar mulki.
Sojojin sun ce sun rufe iyakokin kasar tare da rusa shugabancin hukumomin gwamnatin ta Gabon.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata