DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa Stanley Nkwocha

-

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana Kashim shettima shiga ofishin shugaban kasa a matsayin labari mara tushe bare makama,face son batawa fadar shugaban kasa suna.

Sanarwar Stanley dai ta rawaito cewa an ta yada labarin cewa akwai wani sojoji da aka girke suka hana mataimakin shugaban kasa Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa.

Google search engine

Sanarwa ta kara da cewa ba wani sabon abu bane, domin kuwa ko a farkon wannan makon, an ta yada hotunan allunan yekuwar yakin neman zaben Shugaba Tinubu da Kasshim wanda tuni Fadar Shugaban Kasar ta fito karara ta musanta.

Stanley Nkwocha ya kuma kara da cewa, Mataimakin shugaban kasar ya ci gaba da maida hankali kan ayyukansa,da kuma marawa shugaban kasa baya wajen cimma muradun ‘yan Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara