DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar PDP a shirye take domin tunkarar zaben 2027 – Samuel Anyanwu

-

Sakataren jam’iyyar PDP na kasa, Samuel Anyanwu, ya bayyana jin dadinsa da irin shirye-shiryen da jam’iyyar ke yi gabanin zabukan 2027 a jihar Imo da Nijeriya.

Anyanwu, ya bayyana hakan ne a karshen mako, lokacin da yake jawabi ga kwamitin zartarwar jam’iyyar PDP a jihar Imo, wanda ya hada da shugabanni da masu ruwa da tsaki a sakatariyar jam’iyyar a Owerri, jihar Imo.

Google search engine

Ya ce dole ne ‘ya’yan jam’iyyar su yi aiki kafada da kafada domin cimma burinsu na kwace mulki hannun APC, yana mai cewa zaben gwamna na da muhimmanci ga jam’iyyar domin karbar mulki a jihar Imo.

Anyanwu ya ce mutanen Imo sun gaji da yaudara da gwamnatin yanzu ke yi don haka akwai bukatar a tsaya kai da fata domin yin nasara a zabuka masu zuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sabon shugaban hukumar zaben ya yi alwashin dawo da ingantacce da sahihin zabe a Nijeriya

Sabon shugaban hukumar zaɓen Nijeriya, INEC, Farfesa Joash Amupitan, SAN, ya sha alwashin dawo da sahihanci da amincewar jama’a ga tsarin zaɓe na ƙasar, yana...

Ba ni ke tsoma baki a gwamnatin Kano ko raba kwangiloli ba – Rabi’u Musa Kwankwaso

Jagoran jam’iyyar NNPP kuma tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya karyata zargin da ake yi masa na tsoma baki a harkokin mulkin...

Mafi Shahara