DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu zai dawo Nijeriya a Litinin dinnan – Fadar Shugaban Kasa

-

A yau ne ake sa ran shugaba Bola Tinubu zai dawo Nijeriya bayan ya shafe kusan makonni biyu a kasar Faransa, kamar yadda mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga ya tabbatar.

A wata sanarwa da Bayo Onanuga ya fitar a Litinin dinnan, ya bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai dawo gida a yau.

Google search engine

Tun da farko dai, fadar shugaban kasar ta bai wa ‘yan Nijeriya tabbacin cewa shugaban zai ci gaba da gudanar da harkokin mulkin kasar baki daya a kasar Faransa.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis din da ta gabata, Onanuga ya ce, Shugaban ya bar birnin Paris zuwa birnin Landan, ya kuma ci gaba da tattaunawa da manyan jami’an gwamnati, inda yake sa ido kan muhimman al’amuran kasa, ciki har da umarni ga shugabannin tsaro don magance barazanar da ke kunno kai a wasu sassan kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ƴan Nijeriya sun rage fita kasashen waje neman lafiya karkashin mulkin Tinubu – Rahoton jaridar Punch

Babban bankin Nijeriya, CBN ya bayyana cewa ’yan Nijeriya sun kashe dala miliyan 4.74 wajen neman lafiya a kasashen waje daga Mayu 2023 zuwa Maris...

Jam’iyyar PDP reshen Arewa maso Yamma ta nesanta kanta da Tanimu Turaki a matsayin dan takarar shugabancin jam’iyyar daga yankin

Jiga-jigan jam’iyyar PDP daga yankin Arewa maso Yamma sun nesanta kansu daga amincewar da aka yi da tsohon ministan ayyuka na musamman, Tanimu Turaki, SAN,...

Mafi Shahara