DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu zai dawo Nijeriya a Litinin dinnan – Fadar Shugaban Kasa

-

A yau ne ake sa ran shugaba Bola Tinubu zai dawo Nijeriya bayan ya shafe kusan makonni biyu a kasar Faransa, kamar yadda mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga ya tabbatar.

A wata sanarwa da Bayo Onanuga ya fitar a Litinin dinnan, ya bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai dawo gida a yau.

Google search engine

Tun da farko dai, fadar shugaban kasar ta bai wa ‘yan Nijeriya tabbacin cewa shugaban zai ci gaba da gudanar da harkokin mulkin kasar baki daya a kasar Faransa.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis din da ta gabata, Onanuga ya ce, Shugaban ya bar birnin Paris zuwa birnin Landan, ya kuma ci gaba da tattaunawa da manyan jami’an gwamnati, inda yake sa ido kan muhimman al’amuran kasa, ciki har da umarni ga shugabannin tsaro don magance barazanar da ke kunno kai a wasu sassan kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan majalisar dokoki 6 a Jihar Zamfara sun fice daga PDP zuwa APC

‘Yan Majalisar Dokokin Jihar Zamfara 6 da aka zaɓa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP sun sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki ta APC, suna zargin take...

Kotu ta umurci hukumar EFCC ta gabatar da kwamshinan kudi na jihar Bauchi ga kotu bisa zargin safarar N4.6bn

Kotun Tarayya da ke Abuja ta umurci Hukumar EFCC da ta gabatar da Kwamishinan Kuɗin Jihar Bauchi, Yakubu Adamu, a ranar 30 ga Disamba domin...

Mafi Shahara