Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiBadakalar da aka yi a gwamnatin Abba Gida Gida ta fi wadda...

Badakalar da aka yi a gwamnatin Abba Gida Gida ta fi wadda aka yi a shekaru 8 na Ganduje – Tsohon sakataren gwamnatin Kano

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano Dr Abdullahi Baffa Bichi, ya yi kakkausar suka ga gwamnatin Abba Kabir Yusuf, inda ya zarge ta da yin almundahana da rashawa fiye da na gwamnatin da ta gabata.

A cikin wani faifan bidiyo, Bichi ya yi ikirarin cewa gwamnati mai ci ta tafka kurakurai fiye da lokacin tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, wanda a baya ake zarginsa da cin hanci da rashawa a tsawon mulkinsa na shekaru takwas, a cewar jaridar Dailytrust.

Bichi ya yi nuni da cewa gwamnatin ba za ta kai labari ba a zaben 2027, saboda korafin da ake yi kanta inda ya yi alkawarin fallasa aika-aikar da ake zargin gwamnatin da aikatawa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata