DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu mai iya jan mu wata jam’iyya muna PDP – Sule Lamido

-

Sule Lamido

Tsohon gwamnan jihar Jigawa kuma jigo a jam’iyyar PDP, Sule Lamido, yayi watsi da kiran da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya yi na neman shugabannin jam’iyyar adawa su koma jam’iyyar SDP.

Google search engine

El-Rufai, wanda a kwanakin baya ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC zuwa SDP, ya yi wannan kiran ne a wata hira da BBC Hausa.

Wanda a yayin hirar bai ambaci sunan Sule Lamido ba, ya gayyaci manyan ‘yan adawa da suka hada da Atiku Abubakar, da Peter Obi, da Rotimi Amaechi, da Rauf Aregbesola, domin su dawo jam’iyyar SDP.

Da yake mayar da martani a wata hira ta da BBC Hausa ta yi a ranar Lahadi, Lamido ya yi watsi da gayyatar da aka yi masa a matsayin cin fuska, inda ya ce jam’iyyar PDP ce ta taimaka wajen kafa harsashin siyasar El-Rufai.

Ya kuma bayyana cewa jam’iyyar PDP ita ce ta haifi tsohon gwamnan Kaduna El-Rufai,kuma ba za su bar PDP ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

kungiya a cikin APC ta gargadi shugaban jam’iyyar game da hana gwamnan Filato shiga jam’iyyar APC

Wata ƙungiya mai goyon bayan shugaban ƙasa Bola Tinubu a jam’iyyar APC, mai suna Renewed Hope Advocates for Tinubu 2027, ta gargadi shugaban jam’iyyar na...

Gwamnatin Kamaru ta takaita amfani da intanet yayin da ake zaman dar-dar game da sakamakon zaben shugaban kasa

Gwamnatin ƙasar Kamaru ta takaita amfani da intanet a wasu sassa na ƙasar a ranar Alhamis, yayin da ake zaman dar-dar saboda jinkirin bayyana sakamakon...

Mafi Shahara