DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yaron shago ya yi wa ‘yan mata 10 ciki, daga cikinsu hada diyar ogansa a Anambra

-

Wani matashi ɗan shekara 18, da aka tura don koyon sana’a a jihar Anambra, ya shiga hannun hukuma bayan zargin dirkawa mata 10 ciki a watanni biyar kacal, wanda ya haɗa da ‘yar ubangidansa da abokiyar zamansa a shagon sana’ar.

Kwamishinar Mata da Jin Daɗin Jama’a ta jihar Anambra, Ify Obinabo, ta bayyana hakan a wani faifan bidiyo da ta watsa kai tsaye a kafar sada zumunta a ranar Laraba, lamarin ya faro ne tun bayan da aka tura matashin zuwa koyon sana’a.

Google search engine

Bayan wata uku kacal da fara koyon sana’ar, matashin ya ke bibiyar ‘yar maigidansa da kuma wata zaman shago, lamarin da ya sa aka kori shi daga wurin koyon sana’ar.

Bayan ya koma gari, Kwamishina Obinabo ta ce lamarin ya kara ta’azzara, inda tace uwar yaron ce ta zo ofishinta don neman mafita.

Obinabo ta bayyana cewa bata iya magance lamarin ita kadai ba, ta kuma nemi shawarwari daga jama’a don gano mafita – tana tambayar ko akwai wani al’amari na ruhanai da ke tattare da lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun saurari kiran da aka ba da umarnin kama ni bayan wani ya yi kutsen wayar Ribadu – El-Rufai

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya ce ya saurari wata tattaunawar waya da ya danganta da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA),...

El-Rufai ya zargi gwamnatin Tinubu da hannu a yunƙurin sanya Kwankwaso cikin jerin takunkumin Amurka

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na iya kasancewa a bayan yunƙurin dan Majalisar Dokokin Amurka,...

Mafi Shahara