DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar ADC ta bugi kirjin kayar da gwamnatin APC ta Tinubu a zabe mai zuwa

-

Jam’iyyar African Democratic Congress ADC ta sha alwashin hada akalla masu kada kuri’a miliyan 35 domin kawar da jam’iyyar mai mulki ta APC da kuma Shugaba Bola Ahmed Tinubu idan har ya nemi tazarce a shekarar 2027.

Shugaban jam’iyyar na kasa, Ralphs Okey Nwosu, ne ya bayyana hakan, yayin taron ADC Global Summit da jam’iyyar ta shirya a Abuja.

Google search engine

Nwosu ya yi tambaya kan sahihancin shugabanci da aka samu da kuri’u kasa da miliyan 10, yana mai tunatar da cewa an yi rajistar masu kada kuri’a sama da miliyan 88 a kasar kafin zaben 2023.

Ya ce jam’iyyar ADC na sake tsarinta da karfafa kanta domin fuskantar kalubalen zabe tare da farfado da kwarin guiwar masu kada kuri’a, wanda ya ragu matuka a zabukan baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu babbar kyauta ne daga Allah domin gyaran Nijeriya – Yahaya Bello

Tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya bayyana shugaban Nijeriya Bola Tinubu a matsayin babbar kyauta da Allah ya ba Nijeriya domin gyaran kasar. Yahaya Bello...

Gwamnatin Nijeriya ta ce cin jarabawar lissafi “Mathematics” wajibi ne ga daliban Sakandare kafin kammalawa

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa lallai dukkan ɗalibai masu rubuta jarabawar kammala sakandare su cigaba da rubuta lissafi tare da harshen Turanci a matsayin wajibi. Mai...

Mafi Shahara