Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaMuna goyon bayan tazarcen Shugaba Tinubu a 2027 - Jiga-jigan APC a...

Muna goyon bayan tazarcen Shugaba Tinubu a 2027 – Jiga-jigan APC a Arewa maso Yammacin Nijeriya

Jiga-jigan jam’iyyar APC a Arewa maso Yammacin Nijeriya sun sanar da matsayarsu da ke cewa suna goyon bayan Shugaba Tinubu ya yi tazarce a babban zaben shekarar 2027 da ke tafe.

A taron masu ruwa da tsaki da suka gudanar a Kaduna, jiga-jigan da suka hada da gwamnoni, Sanatoci, masu rike da mukamai a fadar shugaban kasa, sun ce sun gamsu da salon mulkin Shugaba Tinubu, shi ya sa suka amince da ya yi tazarce a zabe mai zuwa.

Daga cikin waɗanda suka halarci taron akwai gwamnonin jihohin Kebbi, Kaduna da Jigawa. Kazalika akwai kuma Sanata Atiku Bagudu, Badaru Abubakar, Sanata Barau Jibrin da Tajuddeen Abbas.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata