Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiDadi nake ji idan na takalo manyan mutane - inji ministan Abuja...

Dadi nake ji idan na takalo manyan mutane – inji ministan Abuja Wike

Ministan birnin tarayya Abuja Nyesom Wike, ya ce yana samun farin ciki duk lokacin da ya takalo manyan mutane a kasar.

Wike, wanda ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da manema labarai a Abuja, ya ce duk masu kadarorin da ke Abuja da har yanzu ba su biya harajin kasa na gidansu ba, inda ya kara da cewa dole ne su yi hakan ko kuma su fuskanci fushin doka.

Tsohon gwamnan jihar Ribas ya caccaki wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP da suka hada da Bode George, yana mai cewa dole ne PDP ta biya harajin ofishinta da ke Abuja.

Wike ya ce magabatansa da suka jagoranci babban birnin tarayya Abuja ciki har da gwamnan jihar Bauchi a yanzu Bala Mohammed, sun kasa tilasta jiga-jigan ‘yan siyasa wadanda suka mallaki gine-gine a Abuja su rika biyan kudin harajin gidajensu na shekara-shekara.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata