Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiAn tsare yaron da ake zargi da ajalin mahaifiyarsa a jihar Osun

An tsare yaron da ake zargi da ajalin mahaifiyarsa a jihar Osun

Wata kotun majistare da ke Osogbo a jihar Osun, ta tasa keyar wani matashi mai suna Taofeek Jimoh a gidan yari na Ilesa bisa zargin hallaka mahaifiyarsa.

Jimoh, wanda ba a ka gurfanar ba tare da lauya mai kare ba, ana tuhumarsa da laifin kisan kai.

Mai gabatar da kara, ASP Fatoba Temitope, ta shaida wa kotun cewa wanda ake kara ya aikata laifin ne da misalin karfe 8 na daren ranar 19 ga watan Fabrairu a Oke-Ola, Osogbo.

Temitope ya ce wanda ake tuhumar ya doki mahaifiyarsa, Taibat Jimoh rauni, bayan wata jayayya da suka yi, kuma hakan ya yi sanadin mutuwarta.

Alkalin kotun, Mista O. Olatunji, ya ce za a ci gaba da tsare Jimoh har zuwa ranar 17 ga watan Yuni, inda za a ci gaba da sauraren karar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata