DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC ta musanta ba ‘yan majalisar dokokin Nijeriya tikitin takara na yin tazarce babu hamayya a 2027

-

Jam’iyyar APC ta musanta rahotannin da ke yawo a kafafen yada labarai da ke cewa ta bai wa dukkanin ’yan majalisar tarayya da ke kan kujeru tikitin tsayawa takara don tazarce ba tare da hamayya ba, tana bayyana irin wannan labari a matsayin “marar tushe bare makama.”

A wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar na kasa, Felix Morka, ya fitar, jam’iyyar APC ta bukaci ’ya’yanta da al’umma gaba daya da su yi watsi da abin da ta kira “rahoton karya da ake ikirarin ya fito daga jam’iyyar.”

Google search engine

Wannan bayani ya fito ne a daidai lokacin da ake kara yada jita-jita game da tsarin zaben fitar da ’yan takarar jam’iyyar gabanin zabe mai zuwa.

Morka ya jaddada cewa duka hukuncin da jam’iyyar za ta yanke za a sanar da su ne ta hanyoyi na hukuma da aka tabbatar da sahihancinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yawaita buga sabbin takardun kudi da da aka rika yi a gwamnatin Buhari ne ya gurgunta darajar Naira – Oshiomhole

Sanata Adams Oshiomhole, ya zargi tsohuwar gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da taka raws wajen gurgunta tattalin arziki Nijeriya Ya bayyana hakan a wani taro...

Murabus din Ganduje wata maƙarƙashiya ce aka shirya domin cire Shettima daga gwamnatin Tinubu – Zargin wasu mutanen Borno

Wasu daga cikin al'ummar jihar Borno sun zargi murabus din Ganduje a matsayin wata maƙarƙashiya da aka shirya domin a kawar da Kassim Shettima a...

Mafi Shahara