Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnatin jihar Neja ta dakatar da bukukuwan Sallah na don jimamin wadanda...

Gwamnatin jihar Neja ta dakatar da bukukuwan Sallah na don jimamin wadanda ambaliyar ruwa ta shafa

Gwamnan jihar Neja Umar Bago ya dakatar da duk wasu tarukan Sallah da suka hada da Hawan Bariki, da sauran tarukan jama’a da ake yi a yayin bikin sallah.

A cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar, Abubakar Usman ya fitar a ranar Laraba, ya ce wannan umarni na zuwa ne biyo bayan mummunar ambaliyar ruwa da ta afku a Mokwa, inda iyalai da dama suka rasa matsugunansu tare da rasa rayukansu.

Sanarwar ta ce an dauki wannan matakin ne a matsayin taya jimami ga wadanda ibtila’in ambaliyar ruwa ya shafa a Mokwa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata