DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mune ‘ya’yan jam’iyyar NNPP ta asali, Alhassan Rurum yayi fatali da dakatarwar da jam’iyyar NNPP ta yi masu a Kano

-

Dan majalisa mai wakiltar mazabar Rano, Kibiya, da Bunkure a majalisar wakilan Nijeriya, Hon. Kabiru Alhassan Rurum, ya yi watsi da dakatarwar da aka yi masa daga jam’iyyar NNPP a Jihar Kano.

Da yake mayar da martani kan sanarwar dakatarwar da shugaban jam’iyyar NNPP na jihar Kano, Hashim Sulaiman Dungurawa ya fitar, Kabiru Alhassan Rurum ya ce shi da takwarorinsa da aka dakatar ba su taba bin bangaren da suka sauya tambarin jam’iyyar ba, yana mai jaddada cewa suna cikin jam’iyyar ta asali.

A baya dai Alhassan Rurum da Aliyu Sani Madakin Gini sun fito fili sun ware kansu daga tafiyar Kwankwasiyya tare da jaddada kansu a cikin Jam’iyyar NNPP mai alamar kayan marmari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rukunin farko na maniyyatan jihar Bauchi a Nijeriya, sun tashi zuwa Saudiyya- NAHCON

Hukumar aikin Hajji ta Nijeriya ta bayyana cewa maniyyata 2,520 ne daga cikin jihar Bauchi za su halarci aikin Hajjin bana na 2025 a kasar...

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su...

Mafi Shahara