Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce jam’iyyar APC tana maraba da ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike a duk lokacin da ya yanke shawarar sauya sheka zuwa jam’iyyar.
Shugaban ya bayyana haka ne a lokacin da ya kaddamar da wasu tituna a gundumar Katampe dake Abuja.
Ya ce duk da cewa Wike ba dan jam’iyyar APC bane, amma jam’iyyar a shirye take ta karbe shi duk sanda ya canza ra’ayi domin ya yi rijista da jam’iyyar.
