Fadar Shugaban Kasa ta ba da hakuri kan kuskuren saka sunayen mutanen da har yanzu suna raye, Pa Reuben Fasoranti da Dr. Edwin Madunagu, a jerin wadanda aka ba lambar yabo bayan rasuwarsu.
A jawabinsa na Ranar Dimokuradiyya ne, Shugaba Bola Tinubu ya ambato sunayen a cikin jerin wadanda suka rasu, lamarin da ya janyo cece-kuce.
Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa hakan kuskure ne kuma za a gyara dukkan bayanan a shafin yanar gizo na gwamnati.
