DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fadar shugaban Nijeriya ta musanta bai wa Aisha Yesufu lambar karramawa

-

Fadar Shugaban Ƙasa ta karyata wani jerin sunaye da ke yawo a shafukan sada zumunta da ke cewa an bai wa Aisha Yesufu da wasu mutum 35 lambar karramawa daga hannun Shugaba Bola Tinubu.

Sunayen da suka fara yawo tun ranar Juma’a sun jawo ce-ce-ku-ce a tsakanin ‘yan Najeriya, musamman magoya bayan gwamnatin Tinubu, sakamakon saka sunan Aisha Yesufu, fitacciyar ‘yar fafutukar kare haƙƙin ɗan adam da ke sukar gwamnati akai-akai.

Google search engine

A ranar Alhamis, 13 ga Yuni, Shugaba Tinubu ya bayyana sunayen mutane 66 da aka karrama a jawabinsa na Ranar Dimokuraɗiyya da ya gabatar a gaban zaman hadin gwiwar Majalisar Tarayya da ke Abuja, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Mai taimaka wa Shugaban Tinubu kan harkokin yada labarai, Temitope Ajayi, ta ce sunayen da ke yawo ba na gaske ne ba kuma ba su da alaƙa da fadar Shugaban Ƙasa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC na duba buƙatun kungiyoyi 110 da ke neman rigista a matsayin jam’iyyun siyasa a Najeriya

Hukumar zabe ta kasa INEC ta bayyana cewa ta karɓi wasikun buƙatun rajistar sabbin jam’iyyu 110 daga kungiyoyi daban-daban har zuwa Litinin, 23 ga watan...

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam’iyyar na kasa

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam'iyyar na kasa Jam’iyyar PDP ta dawo da Samuel Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyya na kasa bayan...

Mafi Shahara