Abdulmannan Abubakar Giro Argungu ya rasu a wannan Asabar, kusan shekaru biyu bayan rasuwar mahaifinsa.
Matashin shi ne da na tara cikin‚ ‘ya’yan babban malamin addinin Musulunci, Marigayi Sheikh Abubakar Giro Argungu.
A wata hira da DCL Hausa ta yi da shi a 2024, matashin, ya ce ya koyi gudun duniya da riko da addini daga mahaifinsa wanda ya rasu a watan Satumba na 2023
Abdulmannan ne dai ke jagoran masu kula da shafin sada zumunta na marigayi Sheikh Abubakar Giro.
Matashin da ya kammala karatun digirinsa jami’ar Maryam Abacha ya rasu ne bayan fama da gajeruwar jinya. An jima da karfe 2:30pm ake sa ran yi masa jana‘iza a garin Argungu, jihar Kebbi.