Shugaban rundunar sojin ƙasa, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ya bukaci sabbin sojoji da suka kammala karbar horo a makarantar horon aikin soja “Depot Nigerian Army” da ke Zariya, Jihar Kaduna, da su kimtsa domin yakar ta’addanci da ’yan tawayen da ke addabar ƙasar.
A jawabinsa ga sabbin sojoji 6,195, Oluyede ya ja hankalinsu da su kasance jarumai, masu aiki da kwarewa kuma masu juriya a fagen daga.
Ya tunatar da su cewa rayuwar soja tana buƙatar sadaukarwa da kishin ƙasa, yana mai nanata cewa aikinsu ne kare martabar Nijeriya.
Oluyede, ya kuma jaddada muhimmancin kiyaye dabi’un rundunar soji irin su ladabi, biyayya, gaskiya, sadaukarwa, jaruntaka da mutunta jama’a.

Comment:masha allah