Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiWike ya jagoranci wasu tsofaffin gwamnonin PDP don ganawa da Tinubu

Wike ya jagoranci wasu tsofaffin gwamnonin PDP don ganawa da Tinubu

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya gana da wasu fitattun ’yan jam’iyyar adawa ta PDP a fadarsa da ke Aso Rock a daren Asabar.

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ne ya jagoranci abokan siyasarsa da suka haɗa da tsoffin gwamnonin G5, waɗanda suka ƙi juyawa PDP baya a zaɓen 2023.

A wancan lokaci, G5 karkashin jagorancin Wike sun yi watsi da Atiku Abubakar, ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP, inda suka goyi bayan Tinubu na jam’iyyar APC.

Jaridar punch ta ruwaito cewar tsoffin gwamnonin da suka halarci taron sun haɗa da Ayodele Fayose na Jihar Ekiti, Samuel Ortom na Benue, da Okezie Ikpeazu na Abia.

Ko da yake ba a bayyana cikakken abin da aka tattauna ba, rahotanni sun nuna cewa sun tattauna hanyoyin haɗin gwiwa da komawa jam’iyya mai mulki ta APC, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata