Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiDaliban jami'ar ABU sun yi nasara a gasar kotun ECOWAS ta farko...

Daliban jami’ar ABU sun yi nasara a gasar kotun ECOWAS ta farko da aka gudanar a Neja

Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya (ABU) ta lashe gasar Kotun ECOWAS ta farko da aka shirya, inda ta samu kambin zakara tare da kyautar naira miliyan 5.

Gasar ta kunshi manyan makarantu takwas da ke da bangaren karatun aikin lauyan, kuma ɗaliban ABU sun nuna kwarewa da fahimta mai zurfi a muhawara da zaman kotu har suka fi kowa fice a zagayen ƙarshe.

Jami’ar Jos ce ta zo ta biyu a gasar, inda ta samu kyautar naira miliyan 3, a yayin gasar da aka gudanar a jihar Neja a ranar Asabar.

Shugaban Kotun ECOWAS, Ricardo Gonçalves, ya jinjinawa dukkan mahalarta gasar, yana mai cewa wannan gasa ta bayyana irin zurfin ilimi da kwazon matasan lauyoyi a yankin Afirka ta Yamma.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata