DCL Hausa Radio
Kaitsaye

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

-

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa a ranar 30 ga Yuni, tana mai cewa sanarwar ta saba ka’idoji.

A wata wasika da INEC ta aike wa jam’iyyar, mai dauke da sa hannun mataimakiyar sakatariyar hukumar, Hajiya Hau’ru Aminu, an bayyana cewa sanarwar bata cika sharuddan da ke sashe na 2(12)(3) na dokokin jam’iyyun siyasa na 2022 ba, wanda ke bukatar shugaban jam’iyya na kasa da sakataren jam’iyya su sanya hannu tare.

Google search engine

INEC ta shawarci PDP da ta bi ka’ida wajen gabatar da irin wannan sanarwa a nan gaba. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da rikice-rikice ke ci gaba da ruruwa a cikin jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara