DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin nasarawa za ta gina sansanonin tsaro a kowane yankin Sanata na Jihar

-

Saboda yawaitar matsalar rashin tsaro, Gwamnatin Jihar Nasarawa ta bayyana shirinta na kafa sansanonin tsaro a kowane daga cikin yankunan sanatoci guda uku na jihar, domin kara inganta zaman lafiya da tsaro.

Daily Nigerian ta ruwaito kwamishinar kudi da tsare-tsare ta jihar, Munira Abdullahi, na bayyana haka yayin taron jin ra’ayin jama’a kan kasafin kudin yankin Nasarawa ta Arewa da aka gudanar a karamar hukumar Keffi, ranar Laraba.

Google search engine

Munira, wadda Babban Sakataren ma’aikatar kudi, Polinus Wahe, ya wakilta, ta ce matakin ya biyo bayan korafin jama’a kan bukatar karin tsaro a yankunansu.

Gwamnatin ta ce wannan shiri na daga cikin dabarun da take dauka domin tinkarar kalubalen tsaro a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC ta sanar da za ta gudanar da zabukan cike gurbi a fadin Nijeriya

Hukumar zaben Nijeriya INEC ta bayyana cewa za ta gudanar da zabukan cike gurbi a mazabun da abin ya shafa a ranar Asabar 16 ga...

Gwamnatin Kaduna ta yi watsi da ikiranin da El-Rufai ya yi kan ayyukan da Tinubu ya kaddamar cewa shi ne ya fara su

Gwamnatin jihar Kaduna ta yi watsi da ikirarin da wani tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai ya yi na cewa dukkanin ayyukan da shugaban kasa Bola...

Mafi Shahara