DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matatar Dangote ta shigo da danyen mai ganga miliyan 3.65 cikin watanni biyu – Jaridar Punch

-

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote, ya ce matatarsa ta fara dogaro da Amurka wajen samun danyen mai saboda ba ta samu isasshe a nan cikin gidan

Dangote ya bayyana haka ne a lokacin da ko’odinetar kwamitin kula da cinikin danyen mai da kudin Naira na Shugaba Tinubu, Maureen Ogbonna, ta jagoranci wata tawaga zuwa matatar.

Google search engine

Aliko Dangote ya yabawa kwamitin kan rawar da suke takawa wajen ganin an aiwatar da yarjejeniyar canjin danyen man fetur da kudin Naira, sai dai ya ce saboda karancin danyen mai a cikin gida, matatar na kara dogaro da shigo da shi daga Amurka don biyan bukatunta a cikin ‘yan watannin nan.

Wannan ya zo ne a daidai lokacin da binciken jaridar Punch ta yi hasashen cewa matatar man Dangote za ta shigo da jimillar gangar danyen mai miliyan 17.65 tsakanin watan Afrilu zuwa Yulin 2025, inda tuni ya shigo da kusan ganga miliyan 3.65 a cikin watanni biyun da suka gabata.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC na duba buƙatun kungiyoyi 110 da ke neman rigista a matsayin jam’iyyun siyasa a Najeriya

Hukumar zabe ta kasa INEC ta bayyana cewa ta karɓi wasikun buƙatun rajistar sabbin jam’iyyu 110 daga kungiyoyi daban-daban har zuwa Litinin, 23 ga watan...

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam’iyyar na kasa

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam'iyyar na kasa Jam’iyyar PDP ta dawo da Samuel Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyya na kasa bayan...

Mafi Shahara