Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa ba ta yadda Shugaba Tinubu zai sake cin zabe a shekarar 2027 domin abu ne da ba zai yiwu ba.
A cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa X a ranar Alhamis, El-Rufai, wanda jigo ne a jam’iyyar SDP, ya bayyana cewa al’umma sun gaji da mulkin jam’iyyar APC, kuma sun cire tsammani kan gwamnatin yanzu.
Nasiru El-Rufai ya ce duk wanda ke tunanin za a sake zaben Shugaba Bola Tinubu yana rayuwa ne a wata ƙasa daban, ba Najeriya ba, domin babu wata hanya da za ta kai shi ga nasara.