DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kalaman Abubakar Malami SAN kan lamarin tsaro siyasa ce tsantsa – Gwamnatin jihar Kebbi

-

Gwamnatin jihar Kebbi ta nuna rashin jin dadinta kan kalaman da tsohon ministan shari’a kuma babban lauyan gwamnatin tarayya, Abubakar Malami, SAN ya yi, inda ta zarge shi da sanya siyasa cikin al’amuran tsaro.

Malami dai ya yi zargin cewa an halaka akalla mutane 200 a wani harin ‘yan bindiga da suka kai kwanan nan a Masarautar Zuru, ikirarin da gwamnatin jihar ta yi watsi da shi ta ce kalamai ne kawai na son rai.

Google search engine

A jawabansu da suka fitar kwamishinan yada labarai da al’adu na jihar, Yakubu Ahmad da kuma mai bai wa gwamnan shawara na musamman kan harkokin yada labarai Yahaya Sarki, sun bayyana kalaman Abubakar Malami a matsayin shaci fadi inda suka yi zargin cewa yanayinsu ne domin samun karbuwa a siyasance.

Kwamishinan ya bayyana cewa daga shekarar 2015 zuwa 2023,Malami ya rike daya daga cikin manyan ofisoshi a Nijeriya a matsayin Atoni Janar a karkashin tsohon Shugaba Muhammadu Buhari, amma duk da haka a lokacin, Zuru da sauran sassan jihar Kebbi sun sha fama da hare-haren ‘yan bindiga, ba a taba samun labarin ya kai ziyara ko aiko wasika domin yin jaje ko ta’aziyya ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An karrama daraktan Rediyon Jigawa a ƙasar Saudiyya bisa dawo da kuɗin wani da ya tsinta.

Wani ma’aikacin gudanarwa a Saudiyya, Muhammed Salalah, ya mika kwafin Alkur’ani Mai Tsarki ga Daraktan Rediyon Jigawa, Malam Isma’il Babura, a matsayin kyauta mai daraja...

Rundunar ‘yan sanda ta kama mutane 53 kan tagwayen hare-hare a jihohin Benue da Filato – IGP Egbetokun

Sufeto janar na ‘yan sandan Nijeriya, Kayode Egbetokun, ya bayyana cewa an kama mutane 53 da ake zargi da hannu a hare-haren da suka yi...

Mafi Shahara