DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar Sanatocin Arewa ta yi tir da kisan da aka yi wa wasu matafiya 12 da suka fito daga jihar Kaduna

-

Kungiyar Sanatocin Arewa ta yi Allah-wadai da ajalin matafiya 12 ‘yan jihar Kaduna da wasu suka yi a jihar Filato yayin da suke tafiya daurin aure a karamar hukumar Pan da ke jihar.

A cikin wata sanarwa da ya fitar Litinin dinnan, Shugaban kungiyar Sanata Abdulaziz Musa Yar’Adua, ya bayyana harin a matsayin rashin rashin imani, yana mai jaddada cewa irin wannan mummunan tashe-tashen hankula na bukatar gaggauta yin abinda ya dace a kansu.

Google search engine

Ya jaddada cewa irin wannan kisa na rashin hankali da ake yi wa ‘yan kasa wayanda ba su ji ba ba su gani ba, abu ne da ba za a amince da shi ba, don haka akwai bukatar a dauki matakin gaggauwa dan kaucewa ci gaba da faruwar hakan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna da hujja ba a makance muke goyon Tinubu ba – Kungiyar Disciples of Jagaban

Kungiyar magoya bayan shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ta Disciples of Jagaban ta ce ba a makance ta ke nuna goyon baya ga shugaban ba,...

Rundunar sojin Nijeriya ta sulhunta kabilun da ke rikici a Taraba

By Salisu Ado Sulaiman Rundunar sojin kasan Nijeriya ta jagoranci zaman sulhu tsakanin kabilun da ke rikici a jihar Taraba. Kwamandan rundunar Operation Whirl Punch Brigadier Janar...

Mafi Shahara