Ministan birnin tarayya Abuja Nyesom Wike, ya ce manyan mutane da ke zaune a Abuja su ne babbar matsalar birnin saboda son rai da suke nunawa wajen biyan haraji.
Wike ya bayyana haka ne a yayin kaddamar da wasu sabin hanyoyi a Abuja, da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta yi don cika shekara biyu a kan karagar mulki.
Ministan ya ce manyan mutanen da ke zaune a Abuja ba sa son biyan haraji sai dai abin takaici suna biyan kudin haya bisa radin kansu a Landan da Amurka da sauran kasashen waje.