Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiAn kama mutane 22 kan harin da aka kai wa ’yan Kaduna...

An kama mutane 22 kan harin da aka kai wa ’yan Kaduna a jihar Filato – Gwamna Uba Sani

Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya bayyana cewa an kama mutane 22 da ake zargi da hannu a kisan wasu ‘yan asalin jihar su 12 a jihar Filato a ranar Asabar da ta gabata.

Gwamnan ya bayyana haka ne a ranar Litinin a lokacin da ya ziyarci wadanda harin ya rutsa da su a asibitin sojoji na 44 da ke Kaduna.

Ya ce yana ci gaba da tattaunawa da gwamnan Filato Caleb Mutfwang da kuma shugaban kasa Bola Tinubu domin ganin an hukunta duk wadanda ke da hannu a harin.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata