Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiHukumar zabe INEC da jam'iyyar PDP za su gana kan taron NEC...

Hukumar zabe INEC da jam’iyyar PDP za su gana kan taron NEC a yau Talata

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Nijeriya INEC da jam’iyyar PDP za su yi wani zama don magance rikici tsakaninsu kan taron kwamitin zartaswa na jam’iyyar da aka shirya gudanarwa a ranar 30 ga watan Yuni.

Wannan dai na zuwa ne bayan takaddamar da ta kunno kai a tsakanin bangarorin biyu kan rashin bin ka’idojin gudanar da taron, a cikin wasikar da shugaban jam’iyyar PDP na kasa ya tura wa INEC mai dauke da sa hannun Ambasada Umar Damagum ya sanya wa hannu kawai.

A cikin wata wasika da ta aike wa Damagum, INEC ta tabbatar da cewa za ta yi taro da shugabannin jam’iyyar a yauTalata, a dakin taro na hukumar da ke Abuja.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata