DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za mu yi zanga-zanga tsirara idan ba a biya mana bukatunmu ba – Matan jihar Cross Rivers

-

Mata da matasan al’ummar Bendeghe Ekiem da ke ƙaramar hukumar Etung a Jihar Cross River sun ba Kwamishinan Noma, Johnson Ebokpo, wa’adin kwanaki 14 da ya janye shirin sayar da gonar gwamnati da ake shirin yin ruf da ciki, ko kuma su kasance cikin shiri don ganin mata sun yi tsirara su fita su yi rawa a cikin gonar koko.

An yanke wannan shawara ne a ranar Asabar yayin wata zanga-zanga da matasa da mata na al’ummar suka shirya domin nuna rashin jin daɗinsu game da batun.

Google search engine

A wata hira da jaridar PUNCH shugabar mata ta al’ummar, Ntunkai Obi, da kuma jagorar mata Helen Ogar, sun roƙi kwamishinan da ya tuntubi shugabannin al’ummar don su tattauna a kan batun, domin a tantance matakin da ya kamata a ɗauka na gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara