Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiKotu ta sanya ranar yanke hukunci kan bukatar Yahaya Bello ta fita...

Kotu ta sanya ranar yanke hukunci kan bukatar Yahaya Bello ta fita kasar waje domin yin jinya

Babbar Kotun Abuja ta sanya ranar 17 ga Yuli domin yanke hukunci kan bukatar da tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, ya shigar don neman izinin fita kasar waje domin neman lafiya.

Mai shari’a Maryanne Anenih ce ta bayyana ranar, bayan sauraron hujjoji daga bangarorin masu kara da masu kariya a zaman kotun da aka yi ranar Talata.

Yahaya Bello na fuskantar shari’a ne tare da wani Umar Oricha, tsohon daraktan fadar gwamnatin Kogi da wani Abdulsalami Hudu kan tuhume-tuhume 16 da hukumar EFCC ke yi musu, ciki har da karkatar da dukiyar al’umma da ta kai Naira biliyan 110.4 da kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata