Dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour a zaɓen 2023, Peter Obi, ya bayyana cewa har yanzu yana cikin jam’iyyarsa ta LP, duk da kasancewarsa cikin sabuwar hadakar ’yan adawa da ke shirin kalubalantar Tinubu a zaɓen 2027.
Obi ya ce bai sauya sheƙa daga jam’iyyar Labour zuwa jam’iyyar ADC ba, wacce aka zaɓa a matsayin dandalin haɗakar ’yan adawa.
Ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen ɗan takarar gwamnan jam’iyyar Labour a jihar Anambra, Dr George Moghalu, da mataimakiyarsa, Lady Ifeoma Okaro, domin zaɓen gwamna da za a gudanar ranar 8 ga Nuwamba, 2025.
Peter Obi ya ƙara da cewa dukkan mambobin jam’iyyar Labour, har da ’yan majalisar tarayya da aka zaɓa, suna cikin wannan hadin gwiwa ta ’yan adawa.
Har yanzu ina ckin jam’iyyar Labour, duk da na shiga hadaka – Peter Obi
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
