Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiNatasha ta sake shan alwashin komawa majalisar dattawa a ranar Talata

Natasha ta sake shan alwashin komawa majalisar dattawa a ranar Talata

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ‘yar Majalisar Dattawa daga jihar Kogi da aka dakatar, ta shigar da ƙara ga Majalisar Dattawa tana neman su girmama hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ta bayyana dakatarwar wata shida da aka yi mata a matsayin wuce gona da iri.

Kotun, a hukuncin da ta yanke a ranar 4 ga Yuli, ta umurci majalisar da ta duba yiwuwar dawo da sanatar kan kujerarta, tana mai cewa dakatarwar ta sabawa kundin tsarin mulki da kuma ‘yancin wakilcin jama’arta.

A cikin wata wasiƙa mai kwanan wata 11 ga Yuli, 2025, da lauyoyinta na M.J. Numa & Partners LLP suka tura wa majalisar, Sanata Natasha ta bukaci a cika duka sharuddan hukuncin da Mai Shari’a Binta Nyako ta yanke.

Ta kuma bayyana shirinta na komawa bakin aiki ranar Talata, 15 ga Yuli, 2025, tana mai cewa dakatarwar ta sabawa tsarin mulkin ƙasa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata