Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiBabu wani makirci da zai yi nasara akan Tinubu – Inji Akpabio

Babu wani makirci da zai yi nasara akan Tinubu – Inji Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana cewa babu waninmakirci da zai yi nasara akan Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027, kuma ba zai fuskanci irin kalubalen siyasa da tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya samu ba.

A wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Anietie Ekong, ya fitar ranar Lahadi, Akpabio ya ce yankin Niger Delta ba zai yarda da kowanne shiri na kayar da Tinubu daga mulki ba.

Yayin da yake jawabi a wajen bikin cikar hukumar raya yankin Neja Delta NDDC shekaru 25 a birnin Port Harcourt, Akpabio ya ce mutanen yankin suna goyon bayan sake tsayawar Tinubu a 2027 saboda ayyukan raya kasa da ya aiwatar a yankin.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata