Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiKokarin majalisar dattawa ya sa matsalar tsaro ta yi sauki a Nijeriya...

Kokarin majalisar dattawa ya sa matsalar tsaro ta yi sauki a Nijeriya – Inji Sanata Adaramodu

Majalisar Dattawa ta bayyana cewa matsalolin tsaro da suka haɗa da ‘yan bindiga, ta’addanci da garkuwa da mutane da suka addabi Nijeriya a baya, yanzu suna ci gaba da raguwa.

Mai magana da yawun Majalisar Dattawa, Sanata Yemi Adaramodu, ne ya bayyana hakan yayin wata hira da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) a ranar Lahadi a Abuja.

Adaramodu, wanda shi ne shugaban kwamitin harkokin yaɗa labarai na majalisar, ya ce rundunar soji ta yi kokari matuƙa wajen yaki da rashin tsaro.

Ya ce, “Dalilin da ya sa dakarun soji suka yi nasara shi ne domin majalisa ta tabbatar da cewa an yi kasafin kuɗi yadda ya kamata don samar da makamai, alburusai da kuma kula da jin daɗin sojoji.

Adaramodu ya ce wannan ne ya sa sojoji ke ci gaba da fatattakar ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga kuma barazanar tsaro ta takaita ne a wasu jihohi kaɗan kuma duk da haka ana dakile su.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata