Ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja da kuma na Legas za su kasance a rufe a ranar Talata, 15 ga Yuli, 2025, domin girmamawa da bin umarnin hutun da gwamnatin Najeriya ta ayyana, bayan rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari.
Ofishin Jakadancin Amurka a Najeriya ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da aka wallafa a shafin X dinsu a ranar Litinin.’
Sanarwar ta ce: “Ofishin Jakadancin Amurka a Abuja da na Legas za su kasance a rufe a ranar Talata, 15 ga Yuli, 2025, domin bin hutun da gwamnatin Najeriya ta ayyana don girmama marigayi tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.”
“Dukkanin jadawalin ganawar neman visa da aka tsara a wannan rana za a dage su zuwa wani lokaci na gaba,” in ji sanarwar.
