Wasu daga cikin mata da aka sace a ƙananan hukumomin Rafi da Shiroro na Jihar Neja tun a watan Fabrairu 2024 sun dawo gida daga hannun ‘yan ta’adda, inda da dama daga cikinsu ke da juna biyu ko kuma suka dawo da jarirai.
Rahotanni sun nuna cewa ciki juna biyu da jariran da matan ke ɗauke da su na ‘yan ta’addan da suka tsare su fiye da shekara guda ne, kafin jami’an ‘yan sanda su ceto su makonni baya.
Daily Trust ta ruwaito cewar an gano cewa huɗu daga cikin matan suna cikin mutum 25 da aka sace a kauyen Allawa, a kan hanyar Pandogari-Allawa, yayin da suke dawowa daga kasuwa a watan Fabrairu 2024.
Wasu rahotanni sun ce ‘yan ta’addan sun ɗauko matan da yawansu ya kai 24 daga Palu-Waya a karamar hukumar Shiroro a cikin motocin haya, suna ƙoƙarin mayar da su wani wuri daban.
Amma da suka iso yankin Kagara a karamar hukumar Rafi, wata daga cikin matan ta nemi izinin yin lalura. Lokacin da aka tsaya, sai ta ankarar da jama’a tare da neman taimako wanda hakan ya jawo hankalin jama’a, kuma hakan ne yasa aka ceto su daga hannun barayin da kuma cafke direban da yanzu ke hannun ‘yan sanda.
Wata majiya daga hedikwatar ‘yan sandan Jihar Neja da ke Minna ta tabbatar da cewa a yanzu haka matan na karkashin kulawar rundunar, kuma an gano makamai a cikin jakar ɗaya daga cikin matan.
Haka kuma, majiyar ta tabbatar cewa ɗaya daga cikin waɗanda aka ceto tana cikin ‘yan matan Chibok da aka dade ana nema, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Matan da aka sace a Neja sun dawo da juna biyu da jarirai bayan shekara ɗaya a hannun ‘yan ta’adda
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
