Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiAna fargabar mutane 30 sun hadu da ajalinsu a lokacin da kwale-kwale...

Ana fargabar mutane 30 sun hadu da ajalinsu a lokacin da kwale-kwale ya kife da su cikin kogi a jihar Sokoto

Hukumar bada agajin gaggawa ta Kasa NEMA, tace har yanzu tanaci gaba da aikin ceton mutane bayan kifewar wani jirgin ruwa a jihar Sokoto da yayi sanadiyyar batan gwamman mutane.

A cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar ta bayyana cewa, jirgin wanda ke dauke da fasinjoji sama da 50 da ke a kan hanyarsu ta zuwa kasuwa ya kife ne da safiyar Lahadi.

Hukumar tace a halin yanzu Mutane 10 ne aka iya cetowa, yayin wasu da dama kuma sukai batan dabo da har yanzu ake ci gaba da nemansu.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata