Sunday, April 5, 2026
HomeSiyasaGwamnan Kebbi Nasiru Idris ya naɗa sabon Sarkin Zuru

Gwamnan Kebbi Nasiru Idris ya naɗa sabon Sarkin Zuru

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasiru Idris, ya amince da naɗin Sanusi Mika’ilu-Sami a matsayin sabon Sarkin Zuru.

Mai magana da yawun gwamnan, Ahmed Idris, ya bayyana haka a wata sanarwa da aka fitar a Birnin Kebbi a ranar Alhamis.

Jaridar Daily Nigerian ta ambato kwamishinan harkokin kananan hukumomi da masarautu ta jihar, Garba Umar-Dutsin-Mari, na sanar da naɗin, yayin da ya mika takardar tabbatarwa ga sabon sarki a Zuru.

Kwamishinan ya ce daga cikin ƴan takara uku da suka nemi kujerar, bayan kwamitin zaɓen masarautar ya tantance su, Sanusi Mika’ilu-Sami ne ya samu mafi yawan ƙuri’u da suka ba shi damar hawa gadon sarautar Zurun.

An naɗa shi ne sakamakon rasuwar tsohon Sarkin Zuru, Muhammad Sani-Sami Gomo II, wanda ya rasu a ranar 16 ga Agusta, 2025, a wani asibiti da ke Landan.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata