Ma’aikatar muhalli ta Najeriya ta fitar da gargadin yiwuwar samun ruwan sama mai karfin gaske a jihohi 14, wanda ka iya jawo fuskantar ambaliyar ruwa a wasu sassa.
Cikin wata sanarwa, daraktan da ke kula da sashen zaizayar kasa da kuma ambaliyar ruwa na ma’aikatar Usman Abdullahi Bokani, ya ce an yi hasashen samun ruwan ne daga ranar 4 zuwa 8 ga watan Satumban 2025.
Kazalika ya bukaci masu ruwa da tsaki a dukkanin matakai su kasance cikin shirin ko ta kwana.
Jihohin da sanarwar ta bayyana sun hada da Ebonyi, Cross-River, Kano, Zamfara, Taraba, Abia da kuma Yobe.
Sauran sun hadar da jihohin Plateau, Borno, Imo, Niger, Sokoto, Kaduna da Akwa Ibom.
Ana hasashen ruwan sama mai karfiba jihohi 14
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
