Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) tare da ma’aikatan gwamnatin tarayya sun bukaci a gaggauta duba sabuwar dokar albashin ƙasa, suna mai jaddada cewa albashin Naira 70,000 da ake biya yanzu ba zai iya ɗaukar nauyi ba.
Sun yi wannan kira ne, bayan wasu jihohi da dama a fadin ƙasar suka ɗauki matakin ƙara mafi ƙarancin albashin ma’aikatan su sama da N70,000, domin daidaita da halin tattalin arzikin da ake ciki.
Kungiyoyin kwadago da ma’aikatan da suka zanta da kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) a tattaunawa dabam-dabam, sun ce hauhawar farashi, tsadar abinci, sufuri, gidaje, da sauran aiyukan yau da kullum ya sa N70,000 ba zai iya ɗaukar rayuwa ba.
Shugaba Bola Tinubu dai ya sanya hannu kan sabuwar dokar mafi ƙarancin albashi a watan Yuli 2024, inda ya daga mafi ƙarancin albashin ƙasa daga N30,000 zuwa N70,000.
Albashi mafi kankanta na N70,000 ba zai wadaci ma’aikaci a Nijeriya ba – NLC
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
