DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnonin Nijeriya za su ci gaba da bai wa shugaban kasar goyon baya wajen magance tsaro da ci gaban tattalin arziki-Gwamnan Kwara

-

 

Abdulrahman Abdulrazaq

Google search engine

Shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq, ya yaba wa manufofin tattalin arziki na shugaba Bola Tinubu dake kara habbaka jihohin kasar.

Abdulrazaq ya bayyana hakan ne a ranar Laraba, yayin bikin sabuwar shekara da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima da mambobin kungiyar gwamnonin Nijeriya suka kai wa shugaban kasar a gidansa da ke da ke Legas.

Gwamnan ya kuma bayyana nasarorin da aka samu a harkar noma a karkashin gwamnatin Tinubu, inda ya bayar da misali da yadda aka samu amfanin noma mai yawa a jihar Jigawa.

Abdulrazaq ya baiwa shugaban tabbacin ci gaba da bayar da goyon baya wajen magance kalubalen tsaro da ci gaban tattalin arziki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Ban shirya yin yarjejeniyar sulhu da Iran don kawo karshen yakin da ake yi ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce har yanzu bai shirya yin wata yarjejeniya da Iran domin kawo karshen rikicin da ke kara tsananta tsakanin kasashen...

Mafi Shahara