DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Saturday, April 11, 2026
HomeLabarai‘Yan Nijeriya sun fi jin dadi a yanzu fiye da lokacin samun...

‘Yan Nijeriya sun fi jin dadi a yanzu fiye da lokacin samun ‘yancin kai in ji mai ba shugaba Tinubu shawara kan harkokin tattalin arziki

Mai ba shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu shawara kan harkokin tattalin arziki, Dr. Tope Fasua, ya bayyana cewa duk da matsin tattalin arziki da ake fuskanta a halin yanzu, ’yan Nijeriya suna rayuwa mai inganci fiye da shekarun da aka samu ’yancin kai, 1960.

Fasua ya bayyana haka ne a gidan talabijin na Channels a ranar Juma’a, inda ya ce ba daidai ba ne a rika kwatanta yanzu da shekarun baya lokacin samun ‘yancin kai.

Ya ce gwamnatin Tinubu ta himmatu wajen magance talauci a tsakanin al’umma ta hanyar gyare-gyaren tattalin arziki, saka hannun jari da Samar da ababen more rayuwa ga ‘yan Nijeriya.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata