DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnonin da suka sha suka ta yanzu sun koma jam’iyyar APC – Ministan Abuja Wike

-

Ministan birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ce ficewar wasu gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP zuwa jam’iyyar APC ta tabbatar da goyon bayansa ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Wike ya bayyana haka ne a ranar Laraba yayin kaddamar da wasu ayyuka a Abuja.

Google search engine

Ya ce wasu daga cikin wadannan gwamnonin sun taba zarginsa da rusa jam’iyyar PDP da kuma yi wa APC aiki, amma yanzu sun bar PDP suka koma jam’iyyar da suka dade suna zarginsa da goyon baya,inda yace ya kamata su yaba masa saboda ya yi musu hanya.

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa a cikin kwanaki kalilan da suka gabata, Gwamnan Enugu, Peter Mbah, da Gwamnan Bayelsa, Douye Diri, sun bar PDP suka koma APC tare da wasu ’yan majalisar jiha, lamarin da ya rage yawan gwamnonin PDP daga 11 a zuwa 8 a yanzu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattawan Nijeriya za ta tantance sabon shugaban INEC ranar Alhamis

Majalisar Dattawan Nijeriya ta shirya tantance Farfesa Joash Amupitan, wanda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya zaba domin zama sabon shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, a...

Kashi 8 cikin 100 na ‘yan Nijeriya ne kawai ke iya wanke hannu yadda ya kamata a cewar UNICEF

Asusun tallafawa kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya ce kaso 92 cikin 100 na 'yan Nijeriya ba sa iya wanke hannu yadda ya...

Mafi Shahara