DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba ni ke tsoma baki a gwamnatin Kano ko raba kwangiloli ba – Rabi’u Musa Kwankwaso

-

Jagoran jam’iyyar NNPP kuma tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya karyata zargin da ake yi masa na tsoma baki a harkokin mulkin Jihar Kano ko raba kwangiloli.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a wata hira da BBC Hausa, inda ya ce waɗannan zarge-zargen ba su da tushe, kuma ba ya ganin buƙatar ya mayar da martani ga masu adawa da shi.

Google search engine

Madugun darikar Kwankwasiyyar ya kara da cewa, gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf shi ne ke tafiyar da mulkinsa gaba ɗaya, kuma shi ne aka zaɓa da cikakken nazari tun bayan zaɓen 2019 kuma yanzu yana aiki cikin gaskiya da natsuwa, mu kuma mun ba shi dama ya yi aikinsa.

Tsohon gwamnan ya kuma musanta zancen cewa akwai rikici a jam’iyyar NNPP, yana mai cewa masu yada irin wannan magana ba ‘yan siyasa na gaskiya ba ne kamar yadda jaridar Daily Trust ta wallafa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara